Hare-haren 'Yan Bindiga a Karamar Hukumar Batsari Sun Yi Sanadiyyar Mutuwar Jama'a da Garkuwa da Wasu

top-news

Zaharaddeen Ishaq Abubakar, Katsina Times 

A daren 31 ga Yuli, 2024, hare-haren 'yan bindiga a Karamar Hukumar Batsari sun yi sanadiyyar mutuwar jama'a da garkuwa da wasu a wurare guda uku daban-daban.

Garin Gajen Haro:
Misalin ƙarfe 11:30 na dare, 'yan bindiga sun kai hari a Gajen Haro, inda suka kashe mutane biyar, suka ji wa uku rauni, sannan suka yi garkuwa da mutane biyar. Wannan al'amari ya bar al'ummar cikin jimami da bakin ciki.

Garin Dan Agali:
 Haka zalika, misalin ƙarfe 11:00 na dare, an kuma kai hari a garin Dan Agali. A wannan harin, an kashe mutum daya, an ji wa mutum daya rauni, sannan 'yan bindigar sun yi garkuwa da mutane biyar. Al'ummar garin na cikin halin kunci bayan wannan hari.

Garin Madaddaban Garba:
Harin na farko a daren ya faru ne a garin Madaddaban Garba misalin ƙarfe 10:30 na dare. 'Yan bindiga sun kashe mutane biyu, sun ji wa mutane takwas rauni, sannan sun yi garkuwa da mutane biyu. Al'ummar garin na cikin tashin hankali da damuwa bayan wannan hari.

Wadannan hare-hare sun nuna yadda matsalar tsaro ke kara ta'azzara a Karamar Hukumar Batsari, yayin da 'yan bindiga ke ci gaba da aikata munanan laifuka da garkuwa da mutane.

NNPC Advert